An Bai wa Jiragen Ruwa 33 Izinin Wucewa Ta Mashigar Hormuz Cikin Awanni 24

An Bai wa Jiragen Ruwa 33 Izinin Wucewa Ta Mashigar Hormuz Cikin Awanni 24

Kamfanin dillancin labarai na Iran, IRNA, ya ruwaito cewa rundunar ruwa ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran (IRGC Navy) ta sanar da cewa an bai wa karin jiragen ruwa na kasuwanci guda 33 izinin ratsawa ta mashigar Hormuz cikin awanni 24 da suka gabata, cikin haÉ—in gwiwa da sauran rundunonin ruwa na Iran.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar Lahadi, ta ce jiragen da aka bai wa izinin sun haɗa da tankokin dakon mai, jiragen dakon kwantena da sauran jiragen kasuwanci, waɗanda suka ratsa wannan muhimmin mashigin ruwa ƙarƙashin cikakken tsaro daga Iran tun daga safiyar Asabar.

Sanarwar ta bayyana cewa, bayan rashin tsaron da ya biyo bayan hare-haren sojin Amurka a yankin, rundunar ruwa ta IRGC na ci gaba da sanya ido tare da kula da mashigar Hormuz cikin tsanaki domin tabbatar da tsaron zirga-zirgar kasuwancin duniya.

Mashigar Hormuz, wadda take daga cikin manyan hanyoyin jigilar makamashi a duniya, ta fuskanci tsaiko bayan Amurka da Ƙasar Mamaya suka ƙaddamar da abin da Iran ta kira harin yaƙi ba tare da wani dalili ba a kanta a ranar 28 ga Fabrairu.

Tehran ta sha jaddada cewa matsalolin tsaro a wannan mashigin ruwa, wanda ke haɗa Tekun Fasha da Tekun Oman, sun samo asali ne daga matakan tsokana da Amurka da Ƙasar Mamaya suka ɗauka. Iran ta kuma ce ita da Oman ne ke da alhakin tabbatar da hanyoyin da za su tabbatar da tsaron wucewar jiragen ruwa a yankin.

Post a Comment

0 Comments